Karyewar jari da damfara da miyagun mafarke-mafarke, shan talgen tuwo da gurɓataccen ruwa da kuma murnar shaƙar iskar 'yanci daga bisani, su ne abubuwan da har yanzu ke cikin zukatan wasu fasinjojin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da 'yan Boko Haram suka sace, shekara ɗaya da ta wuce.
Ɗaya daga cikin fasinjojin 64, Mukhtar Bala Mohammed ya ce bai taɓa zaton zai kuɓuta ya koma cikin iyalinsa da rayuwa ba.
"Har yanzu idan na ji ƙarar jirgi, sai na firgita, na ruga da gudu," in ji shi.
Mummunan hari ne da ya yi matuƙar tada hankalin Najeriya da dugunzuma 'yan ƙasar tun bayan sace 'yan matan Chibok a 2014 da jerin satar gomman ɗalibai 'yan sakandire a jihohin Katsina da Zamfara da Kebbi da kuma Kaduna.


0 Comments